مَا لِي سِوَاكْ هَمْ وَأَنْتَ تَعْلَمْ
Ba ni da wani tunani sai kai, kuma ka sani.
Ha
Ha
مَا لِي سِوَاكْ هَمْ وَأَنْتَ تَعْلَمْ
فَالْقُرْبُ مَغْنَمْ وَالْبُعْدُ مَغْرَمْ
Ba ni da wani buri sai Kai, kuma Kai ne Masani
Kusanci da Kai riba ne, nisa kuwa hasara ce
خُذْنِي إِلَيْكَ بَيْنَ يَدَيْكَ
حُسِبْتُ عَلَيْكَ فِي كُلِّ مَا أَعْلَمْ
Ka kai ni gare Ka, a gaban Ka
An kirga ni a matsayin naka a cikin dukkan abin da na sani
أَنْتَ مُرَادِي فَكُنْ لِيْ هَادِي
فَالْقَلْبُ صَادِي فَزِلْ لِيْ ذَا الْهَمْ
Kai ne muradina, sai Ka kasance mini jagora
Zuciya na kishirwa, sai Ka yaye mini wannan bakin ciki
مَنْ ذَا يَكُنْ لِي إِنْ لَمْ تَكُنْ لِي
تَرَى لِذُلِّي وَأَنْتَ أَرْحَمْ
Wa zai kasance mini idan ba Ka kasance mini ba
Kana ganin kankanata, alhalin Kai ne Mafi jin kai
كَمْ ذَا أُنَادِي يَا خَيْرَ هَادِي
يَكْفِي بُعَادِي فَالْجُودُ قَدْ عَمْ
Sau nawa nake kira, ya fiyayyen jagora
Rabuwa ta isa haka, domin karamcin Ka ya game kowa
نُورُ الْوِصَالِ مَهْرُهُ غَالِي
سِوَاكَ مَا لِي جُدْ وَتَكَرَّمْ
Hasken saduwa sadakinsa na da tsada
Ba ni da kowa sai Kai, sai Ka yi kyauta da karamci
قُرْبِي وَبُعْدِي سِيَّانِ عِنْدِي
لِأَنَّ رُشْدِي فِيمَا تَقَسِّمْ
Kusancina da nisana duk daya ne a gare ni
Domin shiryata tana cikin abin da Ka kaddara mini
فَاجْعَلْ هِبَاتِي رُوحَ الْحَيَاةِ
حَبِيبْ ذَاتِي طه الْمُعَلِّمْ
Ka sanya kyaututtukana su zama ruhin rayuwa
Masoyin raina, Taha mai koyarwa
تَعْلَمْ لِقَصْدِي حِبِّي وَوُدِّي
فَكُنْ لِلْكُرْدِي فِي كُلِّ مَغْنَمْ
Ka san nufina, da kaunata da soyayyata
Sai Ka kasance tare da al-Kurdi a kowace riba
صَلَاةُ رَبِّي لِحَبِيبِ قَلْبِي
طه الْمُرَبِّي عَلَيْهِ سَلَّمْ
Salatin Ubangijina ya tabbata ga masoyin zuciyata
Taha mai tarbiyya, amincin Allah ya tabbata a gare shi