اَلْهِجْرَةُ رِحْلَةُ هَادِيْنَا
Hijira Ita Ce Tafiyar Jagoranmu
Ha
Ha
اَلْهِجْرَةُ رِحْلَةُ هَادِيْنَا
حَمَلَ الْإِسْلَامَ لَنَا دِيْنَا
Hijira ita ce tafiyar Jagoranmu
ya zo mana da Musulunci a matsayin addini
فَسَلَامُ اللّٰهِ عَلَی الْهَادِيْ
وَالْكَوْنُ يُرَدِّدُ آمِيْنَا
Amincin Allah ya tabbata ga Jagora
dukkan halitta na nanata "Amin"
رَحَلَ الْصِّدِّيقُ عَنِ الْدَّارِ
فِی صَحْبَةِ خَيْرِ الْأَبْرَارِ
As-Siddiku ya fita daga gidansa
a cikin rakiyar mafificin mutanen kwarai
صَلَوَاتُ اللّٓهِ تُبَارِکُهُ
مَلَأَ الْدُّنْيَا بِالْأَنْوَارِ
Salatin Allah su kasance a gare shi
ya cika duniya da zallan haske
اَللّٰهُ تَكَفَّلَ يَحْمِيْهِ
وَعَلِيٌّ أَصْبَحَ يَفْدِيْهِ
Allah ne ya dauki nauyin kiyaye shi
Aliyu kuma ya sadaukar da kansa gare shi
وَبِسِرِّ الْقَوْمِ الْأَشْرَارِ
بِنْتُ الْصِّدِّيْقِ تُوَافِيْهِ
Da asirin mugayen mutane
'yar As-Siddiku take riske shi
وَصَلَ الْمُخْتَارُ إِلَی طَيْبَةْ
وَ الْكُفْرُ تَرَاجَع فِی خَيْبَةْ
Zababbe ya isa garin Daiba
kafirci kuwa ya ja da baya cikin kaskanci
وَ جُنُوْدُ اللّٰهِ تُحِيْطُ بِهِ
مِنْ نُوْرِ الْاِسْلَامِ الْهَيْبَة
Rundunonin Allah sun kewaye shi
da kwarjini daga hasken Musulunci
بِالْرُّوْحِ سَنَحْمِی الْمُخْتَارا
وَ نُقَاتِلْ عَنْهُ الْكُفَّارا
Da rayukanmu za mu kare Zababbe
kuma mu yaki kafirai dominsa
عَهْدًا لِلّٰـهِ نُبَايِعُهُ
جُنْدًا لِلّٰـهِ وَ اَنْصَارا
Alkawari ne ga Allah muke mubaya'a
a matsayin dakarun Allah da mataimaka